Jarida don Karuwar Musulmi
Allah zai cika haskensa ko da kafirai sun ki ISSN 1595-4471
Juma'a 6 Zulhijjah, 1426
Bugu na 699
Tunatarwa | | Tambaya da AmsaDandalin Siyasa | Hantsi A Takaice kai tsaye | Littafai | Duniya Labari Tattaunawa | Labarai |
|
|
Umurnin hakan ya biyo bayan kiki-kaka da tafiyar hawainiyar da Asusun Da'iratul Amm II yankin na Katsina ke yi ne, wanda ya janyo aka ba su rata don su kammala gina Markazin tasu kafin a ci gaba da yunkurin aiwatar da asusu na Amm II a yankin na Katsina.
Shi dai wannan katafaren ginin Markazin, wanda ko shakka babu bai da na biyu a duk fadin kasar nan a inda ’yan uwa musulmi almajiran Malam Zakzaky suke, ya kunshi masaukin Malam Zakzaky (H) da masu rufa masa baya idan ya zo garin na Katsina, sai matsugunin Wakilin ’yan uwa na garin Katsina Malam Yakub Yahya da iyalansa. Sauran kashi 1\2 na filin kuwa ya kunshi wani katafaren markaz da ke tare da Madrasa (wurin ba da karatu) da dakin komfuta da ke daura da ita Madrasa din.
Sauran filin da ke tattare da Markazin kuwa dakunan aje motoci ne da dakunan Harisawa.
Injiniya mai kula da ginin, Malam Hamisu Imam ya ce a yanzu ginin na bukatar Naira miliyan tara don kammaluwa, bayan ya lashe sama da Naira miliyan goma a baya.
A yanzu dai kule ne ga dukkan ’yan uwa na Katsina na ganin yadda za su ceci wannan matsugunin nasu daga kwacewa da babban Kwamitin Asusu na harka Islamiyya ya ce zai yi.
| Tafsirin Alkur'ani | Hadisai | Crescent International |