Almizan: Jarida don karuwar Musulmi

AlmizanAlmizan logo
Juma'a 15 ga Sha'aban 1435 Bugu na 1133 ISSN 1595-4474


Rahoto

Bala’o’in da ke sauka a kasar nan; Masu aikata miyagun laifuka suka jawo

Cewar Shaikh Dahiru Bauchi a Katsina


 Dahiru Bauchi
Bala'o'in da suke faruwa a halin yanzu cikin wannan kasa, musamman wannan yanki na Arewa, 'yan kasar ne suka jawo shi. Shaikh Dahiru Usman Bauci ne ya bayyana haka, a lokacin da yake karbar wata makaranta da tsohon Shugaban Hukumar PTDF ta kasa, Injiniya Muttaka Rabe, ya gina ya ba Cibiyar Dahiru Usman Bauci ta haddar Alkur'ani mai girma, a ranar wata Lahadi a garin Katsina...

Shehin ya bayyana cewa, sakamakon zagin waliyyai da kafirta juna ne da wasu suke yi, tare da wasu ayyuka na sabo suka fusata Allah, ya sauko mana wannan bala'i.

Ya soki wasu masu fakewa da Darika suna cewa sun yi ‘wusuli,’ suna iya aikata abin da suka ga dama ko da haramun ne, da cewa, ba ma sun bar Darika ba ne, a’a sun ma yi ridda. Domin babu wanda ya isa ya halasta abin da Allah ya haramta.

Ya ce, akwai bukatar su tuba, su dawo cikin Musulmi. Ya yi kira ga jama'a da cewa idan sun ga wanda za ya iya saurara, to a yi masa nasiha, in kuma bai ji nasihar ba, to a kaurace masa, domin ba Musulmi ba ne.

Shehin ya yaba, tare da godiya ga Injiniya Muttaka a kan wannan yunkuri, ya kuma yi fatan Musulmi masu hali su yi koyi da wannan bawan Allah.

A zantawarsa da manema labarai, Injiya Muttaka, ya bayyana godiyarsa ga Allah a kan wannan lamari. Dangane da iyaye kuma, kira ya yi a gare su da su tura yaransu makaranta, domin samun ilimi, tunda shi ne gishirin zaman duniya, kamar yadda Bahaushe yake cewa. “Ilimin addini shi ne babban gishirin zaman duniya ni a gare ni, saboda shi ne ginshikin kowane ilimi da za ka iya samu."

Ya kara da cewa, idan Allah ya taimake ka, kana da ilimin Alkur'ani da Hadisi da sanin yadda za ka bauta wa Ubangijinka, to ko kiyama ta zo maka, ba sai ka yi wata wahala ba. Saboda haka ilimin addini, ilimi ne mai muhimmanci ba ma kamar mu Musulmi.

Ita dai wannan makaranta da take kusa da makarantar tsohuwar ATC da ke gab da kofar Kwaya, Injijiya Muttaka Rabe ne ya gina ta, ya kuma mika ta ga Shaikh Dahiru Bauci, domin ci gaba da karatun haddar Alkur'ani mai girma.


Sanarwa

Sanarwa
Nan filin duk wani sanarwa ne daga duk bangarorin Harka Islamiyyah

    GAYYATA ZUWA MAKON IMAM KHOMEINI
    Imam KhomeiniDandamalin Dalibai da Malamai na Harka Islamiyyah (Academic Forum) na sanar da dukkan ’yan uwa cewa za a yi Makon Imam Khomeini na bana, wanda za a fara daga ranar:
    Juma'a 30 ga Mayu 2014 zuwa Laraba 3 ga Yuni 2014

    Masu Jawabi: Akwai Malamai da masana daban-daban da za su gabatar da lakca, ciki har da Jagoranmu, Sayyid Ibrahim Zakzaky (H)

    Wannan gayyatar na kowa da kowa ne. Allah ya ba da ikon halarta
    Za mu buga jaddawalin nan gaba kadan in sha Allah.


    Labarai cikin hotuna

    Hotunan YAUMUL MAB'AS na bana

    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asMalam Zakzaky yana jawabi
    • Yaumul Mab'asMalam Zakzaky yana jawabi
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron
    • Yaumul Mab'asSashen 'yan uwa a taron