Jarida don Karuwar Musulmi
Allah zai cika haskensa ko da kafirai sun ki ISSN 1595-4471
Juma'a 17 Shawwal, 1426
Bugu na 692
Tunatarwa | | Tambaya da AmsaDandalin Siyasa | Hantsi A Takaice kai tsaye | Littafai | Duniya Labari Tattaunawa | Labarai |
ALMIZAN, ALLAH YA KARE MANA KUAssalamu alaikum. Na bugo ne domin na yaba maku da irin kokarin da kuke yi. Gaskiya muna jin dadin irin yadda kuke kawo mana bayanai filla-filla ba tare da wani son rai ko azarbabi ba. Allah ya yi maku taimako, ya kuma kare mana ku da mu, amin. Daga Alhaji Shu’aibu Mai Fata Kwanar Dangora jihar Kano 0803 964 1849 MUN RIGA MUN RUSA SHIRINKUTo Malamai, watanni uku kenan kuna neman ku hada fitina tsakanin Shi’a da Sunna, har na ji kun yi rabon Aljjana, amma ba ku ba ’yan Shi’a ba, to yanzu dai mun rusa sharrinku, cikin awa uku. Daga 0806 242 1374 ALMIZAN MAKARANTA CEAssalamu alaikum. Al’umma ya kamata mu gane cewa ALMIZAN tamkar wata makaranta ce, wacce in mutum yana karanta ta zai ilmantu, ko da kuwa shi ba musulmi bane. Kodayake sai mai ilimi da hankali da basira ne kadai zai iya gane haka. Daga Muhammad Aruwa Kofar Goga Katsina 0803 692 0810 SIDI SHARIF AL’ALAWAYI HAKA NE?Assalamu alaikum. Sidi Sharif Al’alawi ya haka ne? Mun ga irin taimakon da kake bai wa makarantun Islamiyoyi, Cibiyoyin addini, kungiyoyi da dai-daikun mutanen, amma ga Fudiyoyinmu nan masu yada koyarwar Kakanninka suna bukatar taimako, amma na ji shiru. Ko ba ka san da su bane? Daga Ado NEPA Kofar Waimbai Kurna jihar Kano 0802 437 9973 IYAYEN MANZON ALLAH MUMINAI NEAssalamu alaikum. Yan Salafiyya da Izala ku tuba zuwa ga Allah, iyayen Annabin Rahama (S) Muminai ne ba Mushirikai ba. Yan Aljanna ne, ba kamar yadda kuke riyawa ba. Allah ya kiyashe mu, amin. Daga Abdulwahab Lafiyar Galambi jihar Jigawa 0806 206 8055 AHMADINAJADI MUN GOYI BAYANKADakta Ahmadinajadi mun goyi bayan maganar da ka yi wacce kasashen duniya da kuma kafafen yada labaran Yammacin duniya da masu sharhi daban-daban suke ta yin batsaltsale a kai, suna cewa wai rashin gogewa ce ya sa ka fadi haka, amma mu mun san cewa imaninka ne. Muna yi maka jinjina ta musamman. Hakika ka nuna wa duniya kai mabiyin Imam Husaini ne, kuma ka samu tarbiyya daga wajen dodon Yahudawa, Imam Khumaini. Allah ya kare mana kai da Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Daga Haruna Abba Kazimiyya Computer Center Potiskum jihar Yobe 0803 839 9910 …SHAFE ISRA’ILA SHI NE ZAMAN LAFIYAAssalamu alaikum. Shugaban kasar Iran, Dakta Ahmadnajadi, ni ma na goyi bayanka a kan a shafe haramtacciyar kasar Isra’ila daga taswirar duniya domin dama ba a kan halasci aka kafa ta ba, kasa ce ta ’yan ta’adda da ta’addanci. Don haka shafe ta daga doron duniya shi ne zaman lafiya ga baki dayan al’ummar duniya. Daga Hamza M Djibo Jamhuriyya Nijar (djibohamza@yahoo.fr) …DAKTA AHMADINAJADI YA DACE DA SHUGABANCIN IRANAssalamu alaikum. Lalle Dakta Ahmadnajad ne ya fi dacewa da shugabancin Jamhuriyyar Musulunci ta Iran a wannan zamanin, saboda a ’yan kwanakin da ya yi yana bisa karagar mulkin Iran sai da ya girgiza duk wata gaba ta kafircin duniya. Madalla da wannan shugabanci na Ahmadinajad. Insha Allah sai ka cimma hadafin da ka sa a gaba. Daga Amiru Mu’azu Muhammad Funtuwa jihar Katsina (profnomagic@yahoo.com) KIYAYYAR TA FI KOWACCE MUNIKu sani ya ku iyaye! Hakika kiyayyar da ta fi muni daga kiyayya ga Sahabbai, Tabi’ai, Tabi’an-tabi’un, kai dama ko wanene na daga ababen halitta, ita ce kiyayya ga Ahalin Gidan Annabi (SAAW). Domin kiyayya gare su, kiyayya ce ga Annabi, kiyayya ga Annabi kuma, kiyayya ce ga Allah, ita kuma halaka ne. Ga shi kuma Allah Ya yi umarni cikin Alkur’ani da a so su. Mu kuwa wannan wajibi ne a wurinmu! Muna son su, muna son duk abin da suke so, muna kuma kin duk abin da suke ki! Abin koyi kamar su kuwa, ba mu gani ba. Daga Awwal Sulaiman, G. Dutse, Kano. (awwalusuleiman@yahoo.com) HABA ’YAN IZALA!Assalamu alaikum. Haba ’yan Izala! Idan ana neman hadin kai, ba sukar wani bangare ake yi ba. Daga Adamu Hayin Rigasa Kaduna 0803 287 3662 INA MALAM YAHYA SHARFADI?Assalamu alaikum. Malam Yahya Sharfadi, ka ji tsoron Allah, kuma ka nemi sanin sa a matsayi na hakika. Na tabbatar idan ka yi haka, za ka fahimci yadda al’amuran suke. Daga 0806 567 0981 AMSA KIRAN MALAM ZAKZAKY NE MAFITAAssalamu alaikum. Al’ummar Musulmi ku sani babu zaman lafiya, ko saukin al’amuran rayuwa sai mun yi da’a ga Allah (T). Ga Malami nan na Allah ya kira mu, shi ne Malam Ibraheem Zakzaky, don haka mu karba masa kawai shi ne mafita. Daga 0803 692 0810 ME YA SA BA MA GANIN ALMIZAN A GOMBE?Assalamu alaikum. Mu dai a nan Gombe mun daina ganin ALMIZAN, lafiya dai ko? Daga Ibrahim Mai Soso Je Ka Da Fari Gombe 0802 839 7026 Malam Ibrahim muna kai jarida ALMIZAN Gombe a kowanne sati kamar yadda muka saba, don haka sai ka binciki Malam Dan Yarwa bin Laden don ka samu naka kwafin.-Edaitan Shafi. KIRAN MALAM ZAKZAKY SHI NE HANYAR HADIN KAIAssalamu alaikum. Dakta Ahmad Gumi, kiran Malam Ibraheem Zakzaky shi ne hanyar hadin kai. Don haka ina fatan kai da masu tunani irin naka za ku amsa kiran Malam Zakzaky don sama wa musulmin Nijeriya mafita. Daga 0802 450 8106 ALMIZAN KO KUN MANTA NE?Assalamu alaikum. Don Allah ALMIZAN wai ina batun mai da wasika zuwa ga Malam Shekarau littafi ta kwana ne? Ko dai kun manta ne? Daga Abdulwahab Yankari Experss Bauci 0806 206 8055 MALAM ABUDULJABBAR ALLAH YA SAKA MAKAAssalamu alaikum. Malam Abduljabbar ka ci gaba da fadar gaskiya. A gaskiya Shaikh kana kokari wajen zakulo gaskiya don fadakar da al’ummar musulmi a game da kara sanin tarihin Musulunci. Hakika kwanaki mun ji irin abubuwan da ka fada game da Shi’a a kusa da Unguwar Adakawa. Allah ya saka da alheri. Daga Nura Shitu Idris Kano 0802 861 9629 Assalamu alaikum. Ina sanar da Mustafa Usman Kaduna cewa kalmar la’ilaha illallahu ba a rubuce take ba a aikace take. ’Yan Izala da makamantansu kuwa suna aikata ta ne a aikace. Daga 0802 871 4251
MUN YI MUZAHARAR KUDUS LAFIYA A KANOTo makiya Annabi (S), mun yi muzaharar Kudus kuma an tashi lafiya a Kano, duk da cewa ba haka wadansu suka so ba. Daga Yakubu Nasir Bacirawa Kano (yakubnas@yahoo.com) HADIN KAN MUSULMI, KO HADIN KAN IZALA?Assalamu alaikum. Ina so ne na tambayi Dakta Ahmad Gumi game da hadin kan da yake cewa yana neman ya yi, na musulmi ne, ko kuwa na Izala? Gaskiya dai daya ce; daga kin ta kuma sai bata. Dakta da ka je Zariya ka karo ilimin yadda ake hada kan musulmi. Daga Shu’abu J. Imam Kinkinau jihar Kaduna 0803 287 3959 ALMIZAN HADIN KAI YA DACE KI KOYARAssalamu ala’imu. ALMIZAN hadin kai ya dace ki koyar, domin wallahi yanzu tamkar rana kike, kowa dubarki yake yi. Don haka ki yi kokarin hada kan mutane ba raba su ba. Daga Aliyu Bakir 0806 546 6454 MUNA GOYON BAYAN SHUGABAN IRANIna taya al’ummar musulmin duniya murnar sakon da Shugaban Jamhuriyyar Musulunci ta Iran ya aika ga kafircin duniya, domin a madadin musulmi ya aika. Muna goyon bayansa 100 bisa 100. Domin ko da Hitla ne ya dawo da manufar share haramtacciyar kasar Isra’ila daga bayan kasa, sai mun goyi bayansa, balle Shugaban Iran. Allah ya taimake shi. Daga Mahmud Shehu Tudun Fulani PO BOX 12940 Kano. (mahsheik@yahoo.com) ABIN DA YA KAMATA MATASA SU SANIAssalamu alaikum. matasa ku sani kune kashin bayan ci gaban al’umma, Amma yanzu kun zama kune kaskantattu, kuma koma baya, tamkar bayin mahukunta na wannan kasa, saboda kun ki amsa kiran Ubangiji. Daga Muhammad Kofar Guga Katsina. 0803 692 0810 A GAISHE KU DA AIKIAssalamu alaikum. ALMIZAN ina gai da ku da aiki da kuma fadin gaskiya. Allah ya taimake ku, amin. Daga Arma Gindin Gada, Singa Kano. 0806 554 7469 ALHAJI ALI DATTI YAKO YANA AIKIGaskiya yadda Alhaji Ali Datti Yako yake aiki abin yabawa ne. Da haka Kantomomi suke aiki da sai mu ce Allah ya sa duk Nijeriya a nada Kantomomi. Daga Ishaka (Babban Yaya) Kwanar Dangora, Karamar Hukumar Kiru, Jihar Kano 0803 628 8042 KASASHEN TURAI DA AMURKA KU YI HATTARATsarin tattalin ariziki na Jari-Hujja ba abin da zai haifar sai abin da ake gani yanzu a Faransa. Saboda haka kasashen Turai da Amurka sai a ku yi hattara. Daga Bilyaminu Kiru, Jihar Kano 08023097766 SAI MUN GAMA DA ’YAN SHI’A A KANOKai ja’iri na ga sakonka zuwa ga Shekarau, wanda aka buga a cikin shaidaniyar jaridarku ta wannan satin (18 Ramadan 1426). Mu kam mun san cewa a Sakkwato an sami nasara a kan ’yan Shi’a. Muna fata Allah ya ba mu irin wannan nasarar a kan dukkanku ’yan Shi’a da ke nan Kano da kewaye, mu halaka ku duk. Daga 0802 870 0438 To Malam, kodayake ba ka sanya sunanka da adireshinka na gaskiya ba, ga dukkan alamu ba ka da gaskiya. Muna wata mai alfarma ne, amma ka furta irin wadannan munanan kalaman. To ko ma dai menene ga sakonka nan mun rubuta, sai dai mun cire wuraren da ka yi zage-zage, wannan kuma kai da Ubangijinka. Batun nasara a Sakkwato da ka ce, to ka sake bincike dai. Sannan kuma niyyar da kuke da ita a Kano, kar ku fasa, mafi munin abin da za ku yi mana shi ne mafi alheri a wajenmu.- Editan Shafi |
Shafin Gamji | Tafsirin Alkur'ani | Hadisai | Crescent International |